english
stringlengths
4
2.18k
hausa
stringlengths
3
1.38k
Tell them: "If you think you alone will abide with God to the exclusion of the rest of Mankind, in the mansions of the world to come, then wish for death if what you say is true."
Ka ce: "Idan Gidan Lãhira ya kasance sabõda ku, a wurin Allah keɓe bã da sauran mutãne ba, to, ku yi gũrin mutuwa, idan kun kasance mãsu gaskiya."
But they will surely not wish for death because of what they had done in the past; and God knows the sinners well.
Kuma bã zã su yi gũrinta bahar abada sabõda abin da hannayensu, suka gabãtar. Kuma Allah Masani ne ga azzãlumai.
You will see they are covetous of life more than other men, even more than those who practise idolatry. Each one of them desires to live a thousand years, although longevity will never save them from punishment, for God sees all they do.
Kuma lalle ne, zã ka sãme su mafiya kwaɗayin mutãne a kan rãyuwa, kuma sũ ne mafiya kwaɗayin rãyuwa daga waɗanda suka yi shirka. ¦ayansu yana son dã zã a rãyar da shi shekara dubu, kuma bã ya zama mai nĩsantar da shi daga azãba dõmin an rãyar da shi. Kuma Allah, Mai gani ne ga abin da suke aikatãwa.
Say: "Whosoever is the enemy of Gabriel who revealed the word of God to you by the dispensation of God, reaffirming what had been revealed before, and is a guidance and good news for those who believe, --
Ka ce: Wanda ya kasance maƙiyi ga Jibirilu, to, lalle ne shi ya saukar da shi a kan zũciyarka da izinin Allah, yana mai gaskatãwa ga abin da yake gaba gare shi, kuma da shiriya da bishãra ga mũminai.
Whosoever is the enemy of God and His angels and apostles, and of Gabriel and Michael, then God is the enemy of such unbelievers."
Wanda ya kasance maƙiyi ga Allah da malã'ikunSa da manzanninSa da Jibirĩla da Mĩkã'ĩla to, lalle ne, Allah Maƙiyi ne ga kãfirai.
We have sent clear signs to you, such as none can deny except those who transgress the truth.
Kuma lalle ne haƙĩƙa Mun saukar, zuwa gare ka, ãyõyi bayyanannu, kuma ba wanda yake kãfirta da su fãce fãsikai.
And every time they made a pledge some of them pushed it aside, and many of them do not believe.
Shin, kuma a kõ da yaushe suka ƙulla wani alkawari sai wani ɓangare daga gare su ya, yi jĩfa da shi? Ã'a, mafi yawansu bã su yin ĩmãni.
When a messenger was sent to them by God affirming the Books they had already received, some of them put (His message) behind their backs as if they had no knowledge of it.
Kuma a lõkacin da wani manzo (Muhammadu) daga wurin Allah ya je musu, mai gaskatãwa ga abin da yake tãre da su, sai wani ɓangare daga waɗanda aka bai wa Littãfi, suka yar da Littãfin (Alƙur'ãnin) Allah a bãyan bãyansu, kamar dai sũ ba su sani ba.
And they follow what devilish beings used to chant against the authority of Solomon, though Solomon never disbelieved and only the devils denied, who taught sorcery to men, which, they said, had been revealed to the angels of Babylon, Harut and Marut, who, however, never taught it without saying: "We have been sent to deceive you, so do not renounce (your faith)." They learnt what led to discord between husband and wife. Yet they could not harm any one or without the dispensation of God. And they learnt what harmed them and brought no gain. They knew indeed whoever bought this had no place in the world to come, and that surely they had sold themselves for something that was vile. If only they had sense!
Kuma suka bi abin da shaiɗãnu ke karantawa a kan mulkin Sulaimãnu, kuma Sulaimãnu bai yi kãfirci ba, kuma Shaidãnun, sũ ne suka yi kãfirci, suna karantar da mutãne sihiri. Kuma ba a saukar da shi ba a kan malã'iku biyu a Bãbila, Harũta da Mãrũta. Kuma ba su sanar da kõwa ba balle su ce: "Mũ fitina kawai ne, sabõda haka kada ka kãfirta," balle har su yi ta nẽman ilmin abin da suke rarrabẽwa tsakãnin mutum da mãtarsa da shi daga gare su. Kuma su (mãsu yin sihirin) ba su zama mãsu cũtar da kõwa da shi ba, fãce da iznin Allah. Kuma suna nẽman ilmin abin da yake cũtar da su, kuma bã ya amfaninsu. Kuma lalle ne, haƙiƙa, sun sani, tabbas, wanda ya saye shi, bã ya da wani rabo a cikin Lãhira. Kuma tir da abin da suka sayar da rãyukansu da shi, dã sun kasance suna sani.
Had they come to believe instead, and taken heed for themselves, they would surely have earned from God a far better reward. If only they had sense!
Kuma dã lalle ne sũ, sun yi ĩmani, kuma sun yi taƙawa, haƙiƙa, da sakamako daga wurin Allah shi ne mafi alhẽri, dã sun kasance suna sani.
Say not (to the Prophet), O Believers: "Have regard for us (ra'ina)," but "look at us (unzurna)," and obey him in what he says. Painful is the nemesis for disbelievers.
Yã kũ waɗanda suka yi ĩmani! Kada ku ce: 'Rã'inã' kuma ku ce: 'Jinkirtã manã', kuma ku saurara. Kuma kãfirai suna da azãba mai raɗaɗi.
Those without faith among the people of the Book, and those who worship idols, do not wish that good should come to you from your Lord. But God chooses whom He likes for His grace; and the bounty of God is infinite.
Waɗanda suka kãfirta daga Ma'abuta Littãfi, bã su son a saukar da wani alhẽri a kanku daga Ubangijinku, kuma mushirikai mã bã su so. Kuma Allah Yana keɓance da wanda Yake so da rahamarSa. Kuma Allah Ma'abũcin falala mai girma ne.
When We cancel a message (sent to an earlier prophet) or throw it into oblivion, We replace it with one better or one similar. Do you not know that God has power over all things?
Abin da Muka shãfe daga ãya, ko kuwa Muka jinkirtar da ita, zã Mu zo da mafi alhẽri daga gare ta ko kuwa misãlinta. Ashe, ba ka sani ba, cẽwa lalle ne, Allah a kan dukkan kõme Mai ĩkon yi ne?
Do you not know that God's is the kingdom of the heavens and the earth, and that there is none to save and protect you apart from God?
Shin ba ka sani ba, cẽwa lalle ne Allah, Shĩ ne da mulkin sammai da ƙasa kuma bã ku da, baicin Allah, wani majiɓinci, kuma bã ku da wani mataimaki?
Do you too, O believers, wish to question your Apostle as Moses was in the past? But he who takes unbelief in exchange for belief only strays from the right path.
Kõ kuna nufin ku tambayi Manzonku, kamar yadda aka tambayi Mũsã a gabãnin haka? Kuma wanda ya musanya kãfirci da ĩmãni, to, lalle ne yã ɓace tsakar hanya.
How many of the followers of the Books having once known the truth desire in their hearts, out of envy, to turn you into infidels again even after the truth has become clear to them! But you forbear and overlook till God fulfil His plan; and God has power over all things.
Mãsu yawa daga Ma'abuta Littãfi sunã gũrin dã sun mayar da ku, daga bãyan ĩmãninku, kãfirai, sabõda hãsada daga wurin rãyukansu, daga bayãn gaskiya tã bayyana a gare su. To, ku yãfe, kuma ku kau da kai, sai Allah Yã zo da umurninSa. Lalle ne Allah a kan dukkan kõme Mai ĩkon yi ne.
Fulfil your devotional obligations and pay the zakat. And what you send ahead of good you will find with God, for He sees all that you do ill.
Kuma ku tsayar da salla, kuma ku bãyar da zakka. Kuma abin da kuka gabãtar dõmin kanku daga alhẽri, zã ku sãme shi a wurin Allah. Lalle ne Allah, ga abin da kuke aikatãwa Mai gani ne.
And they say: "None will go to Paradise but the Jews and the Christians;" but this is only wishful thinking. Say: "Bring the proof if you are truthful."
Kuma suka ce: "Bãbu mai shiga Aljanna fãce waɗanda suka zama Yahũdu ko Nasãra." Waɗancan tãtsũniyõyinsu ne. Ka ce: "Ku kãwo dalilinku idan kun kasance mãsu gaskiya."
Only he who surrenders to God with all his heart and also does good, will find his reward with his Lord, and will have no fear or regret.
Na'am! Wanda ya sallama fuskarsa ga Allah, alhãli kuwa yana mai kyautatãwa, to, yana da ijãrarsa, a wurin Ubangijinsa, kuma bãbu tsõro a kansu, kuma ba su zama suna baƙin ciki ba.
The Jews say: "The Christians are not right," and the Christians say: "The Jews are in the wrong;" yet both read the Scriptures; and this is what the unread had said too. God alone will judge between them in their differences on the Day of Reckoning.
Kuma Yahũdãwa suka ce: "Nasãra ba su zamana a kan kõme ba," kuma Nasãra suka ce: "Yahũdãwa ba su zamana a kan kõmeba," alhãli kuwa su, suna karãtun Littãfi. Kamar wancan ne waɗanda ba su sani ba suka faɗa, kamar maganarsu sabõda haka Allah ne ke yin hukunci a tsakãninsu a Rãnar ¡iyãma, a cikin abin da suka kasance suna sãɓawa jũna a cikinsa.
And who is more unjust than he who prohibits the name of God being used in His mosques, who hurries to despoil them even though he has no right to enter them except in reverence? For them is ignominy in the world and severe punishment in the life to come.
Kuma wãne ne mafi zãlunci daga wanda ya hana masallãtan Allah, dõmin kada a ambaci sunanSa a cikinsu, sai kuma ya yi aiki ga rushe su? Waɗannan bã ya kasancẽwa a gare su su shigẽ su fãce suna mãsu tsõro. Suna da, a cikin duniya wani wulãkanci, kuma suna da, a cikin Lãhira, azãba mai girma.
To God belong the East and the West. Wherever you turn the glory of God is everywhere: All-pervading is He and all-knowing.
Kuma Allah ɗai yake da gabas da yamma sabõda haka, inda duk aka jũyar da ku, to, a can fuskar Allah take. Lalle ne, Allah Mawadãci ne, Mai ilmi.
Yet they say that God has begotten a son. May He be praised! Indeed everything in the heavens and the earth belongs to Him, and all are obedient to God.
Kuma suka ce: "Allah Yã riƙi ɗã." Tsarki yã tabbata a gare Shi! A'a, Shi ne da abin da yake a cikin sammai da ƙasa, dukansu, a gare Shi, mãsu ƙanƙan da kai ne.
Creator of the heavens and the earth from nothingness, He has only to say when He wills a thing: "Be", and it is.
Mai kyautata halittar sammai da ƙasa, kuma idan Ya hukunta wani al'amari, sai kawai Ya ce masa: "Kasance." Sai ya yi ta kasancewa.
But those who are ignorant say: "Why does God not speak or show us a sign?" The same question had been asked by men before them, who were like them in their hearts. But to those who are firm in their faith We have shown Our signs already.
Kuma waɗanda bã su da sani suka ce: "Don me Allah bã Ya yi mana magana, ko wata ãyã ta zo mana?" Kamar wancan ne waɗanda suke a gabãninsu suka faɗa, kamar maganarsu. zukãtansu sun yi kamã da jũna. Lalle ne, Mun bayyana ãyõyi ga mutãne masu sakankancewa.
And We have sent you with the truth to give glad tidings and to warn. You will not be questioned about those and who are inmates of Hell.
Lalle ne Mun aike ka da gaskiya, kana mai bãyar da bishãra, kuma mai gargaɗi, kuma bã zã a tambaye ka ba, game da abõkan Wuta.
The Jews and Christians will never be pleased with you until you follow their way. Say: "God's guidance alone is true guidance;" for if you give in to their wishes after having received the (Book of) knowledge from God, then none will you have as friend or helper to save you.
Kuma Yahũdu bã zã su yarda da kõme daga gare ka ba, kuma Nasãra bã zã su yarda ba, sai kã bi irin aƙidarsu. Ka ce: "Lalle ne, shiriyar Allah ita ce shiriya." Kuma lalle ne idan ka bi son zũciyõyinsu a bãyan abin da ya zo maka na ilmi, bã ka da, daga Allah, wani majiɓinci, kuma bãbu wani mataimaki.
Those to whom We have sent down the Book, and who read it as it should be read, believe in it truly; but those who deny it will be losers.
Waɗanda Muka bai wa Littãfi suna karãtunsa a kan haƙƙin karãtunsa, waɗannan suna ĩmani da shi (Alƙur'ãni). Kuma wanda ya kãfirta da shi, to, waɗannan sũ ne mãsu hasãra.
O children of Israel, remember the favours I bestowed on you, and made you exalted among the nations of the world.
Yã Banĩ Isrã'ĩla! Ku tuna ni'imaTa wadda Na ni'imtar da ita a kanku, kuma lalle ne Nĩ, Nã fĩfĩtã ku a kan tãlikai.
Fear the day when no man will stand up for man in the least, and no ransom avail nor intercession matter nor help reach.
Ku ji tsõron wani yini, (a cikinsa) wani rai bã ya tunkuɗe wa wani rai kõme kuma bã a karɓar fansa daga gare shi, kuma wani cẽto bã ya amfanin sa, kuma ba su zama ana taimakon su ba.
Remember, when his Lord tried Abraham by a number of commands which he fulfilled, God said to him: "I will make you a leader among men." And when Abraham asked: "From my progeny too?" the Lord said: "My pledge does not include transgressors."
Kuma a lõkacin da Ubangijin Ibrãhim Ya jarrabẽ shi da wasu kalmõmi, sai ya cika su. Ya ce: "Lalle ne Nĩ, Mai sanya ka shugaba dõmin mutãne ne." Ya ce: "Kuma daga zũriyata." Ya ce: "AlkawarĩNa bã zai sãmu azzãlumai ba."
Remember, We made the House (of Ka'bah) a place of congregation and safe retreat, and said: "Make the spot where Abraham stood the place of worship;" and enjoined upon Abraham and Ishmael to keep Our House immaculate for those who shall walk around it and stay in it for contemplation and prayer, and for bowing in adoration.
Kuma a lõkacin da Muka sanya ¦ãkin ya zama makõma ga mutãne, da aminci, kuma ku riƙi wurin salla daga Maƙãmi Ibrãhĩm, kuma Muka yi alƙawari zuwa ga Ibrãhĩm, da Ismã'ila da cẽwa: "Ku tsarkake ¦ãkiNa dõmin mãsu ɗawãfi da mãsu lizimta da mãsu rukũ'i, mãsu sujada."
And when Abraham said: "O Lord, make this a city of peace, and give those of its citizens who believe in God and the Last Day fruits for food," He answered: "To those will I also give a little who believe not, for a time, then drag them to Hell, a dreadful destination!"
Kuma a lõkacin da lbrãhĩm ya ce: "Yã Ubangijĩna! Ka sanya wannan gari amintacce, Ka azurta mutãnensa, daga 'ya'yan itãcen, wanda ya yi ĩmãni, daga gare su, da Allah da Ranar Lãhira." Allah Ya ce: "Wanda ya kãfirta ma Ina jiyar da shi dãɗi kaɗan, sa'an nan kuma Ina tĩlastã shi zuwa ga azãbar Wuta. Kuma makõmar, ta munana."
And when Abraham was raising the plinth of the House with Ishmael, (he prayed): "Accept this from us, O Lord, for You hear and know everything;
Kuma a lõkacin da Ibrãhĩm yake ɗaukaka harsãshin gini ga ¦ãkin, da Ismã'ĩla (suna cẽwa:) "Yã Ubangijnmu! Ka karɓa daga gare mu, lalle ne Kai, Kai ne Mai ji, Mai sani.
And make us submit, O Lord, to Your will, and our progeny a people submissive to You. Teach us the way of worship and forgive our trespasses, for You are compassionate and merciful;
"Ya Ubangijnmu! Ka sanyã mu, mu biyu, waɗanda suka sallama (al'amari) gare Ka, kuma daga zuriyarmu (Ka sanya) al'umma mai sallamãwa zuwa gare Ka, Kuma Ka nũna mana wurãren ibãdar hajjinmu, kuma Ka karɓi tũba a kanmu. Lalle ne Kai, Kai ne Mai karɓar tũba, Mai rahama.
And send to them, O Lord, an apostle from among them to impart Your messages to them, and teach them the Book and the wisdom, and correct them in every way; for indeed You are mighty and wise.
"Ya Ubangijinmu! Ka aiko, a cikinsu, wani manzo daga gare su, yana karanta musu ãyõyinKa, kuma yana karantar da su Littãfin da hikimar, kuma yana tsarkake su. Lalle ne Kai, Kai ne Mabuwãyi Mai hikima."
Who will turn away from the creed of Abraham but one dull of soul? We made him the chosen one here in the world, and one of the best in the world to come,
Kuma wãne ne yake gudu daga aƙĩdar Ibrãhĩm, fãce wanda ya jãhilta ga ransa? Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun zãɓe shi, a cikin dũniya, kuma lalle ne shi, a cikin Lãhira, haƙĩƙa, yana daga sãlihai.
(For) when his Lord said to him: "Obey," he replied: "I submit to the Lord of all the worlds."
A lõkacin da Ubangijinsa Ya ce masa: "Ka miƙa wuya," ya ce: "Nã miƙa wuya ga Ubangijin tãlikai."
And Abraham left this legacy to his sons, and to Jacob, and said: "O my sons, God has chosen this as the faith for you. Do not die but as those who have submitted (to God)."
Kuma lbrãhĩm ya yi wasiyya da ita ga ɗiyansa, kuma Ya'aƙũbu (ya yi wasiyya, suka ce:) "Yã ɗiyãna! Lalle ne, Allah Ya zãɓã muku addini don haka kada ku mutu, lalle, fãce kuna Musulmi."
Were you present at the hour of Jacob's death? "What will you worship after me?" he asked his sons, and they answered: "We shall worship your God and the God of your fathers, of Abraham and Ishmael and Isaac, the one and only God; and to Him we submit."
Ko kun kasance halarce a lõkacin da mutuwa ta halarci Ya'aƙũbu, a lõkacin da ya ce wa ɗiyansa: "Mẽne ne zã ku bauta wa daga bãyãna?" Suka ce: "Muna bauta wa Abin bautawarka kuma Abin bautawar ubanninka lbrãhĩm da lsmã'ĩla da Is'hãƙa, Ubangiji Guda, kuma mu a gare Shi mãsu miƙa wuya ne."
Those were the people, and they have passed away. Theirs the reward for what they did, as yours will be for what you do. You will not be questioned about their deeds.
Waccan, wata al'umma ce, ta riga ta shige, tana da abin da ta sanã'anta kuma kuna da abin da kuka sanã'anta, Kuma bã zã a tambaye ku ba daga abin da suka kasance suna aikatãwa.
They say: "Become Jews or become Christians, and find the right way." Say: "No. We follow the way of Abraham the upright, who was not an idolater."
Kuma suka ce: "Ku kasance Yahũdãwa ko Nasãra, kwã shiryu."Ka ce: "A'a aƙidar Ibrãhĩm dai, maikarkata, zuwa ga gaskiya, kuma bai kasance daga mãsu shirki ba."
Say: "We believe in God and what has been sent down to us, and what had been revealed to Abraham and Ishmael and Isaac and Jacob and their progeny, and that which was given to Moses and Christ, and to all other prophets by the Lord. We make no distinction among them, and we submit to Him."
Ku ce: "Mun yi ĩmãni da Allah, da abin da aka saukar zuwa gare mu, da abin da aka saukar zuwa ga Ibrãhĩm da Ismã'ĩla da Is'hãka da Ya'aƙũbu da jĩkõki, da abin da aka bai wa Mũsã da Ĩsã, da abin da aka bai wa annabãwa daga Ubangijinsu, bã mu rarrabẽwa a tsakãnin kõwa daga gare su, kuma mu, a gare Shi, mãsu miƙa wuya ne."
If they come to believe as you did, they will find the right path. If they turn away then they will only oppose; but God will suffice you against them, for God hears all and knows everything.
To, idan sun yi ĩmãni da misãlin abin da kuka yi ĩmãni da shi, to, lalle ne sun shiryu, kuma idan sun jũya bãya, to, suna a cikin sãɓãni kawai sabõda haka Allah zai isar maka a gare su, kuma Shi ne Mai ji, Masani.
"We have taken the colouring of God; and whose shade is better than God's? Him alone we worship."
Rinin Allah! Kuma wãne ne mafi kyau ga rini daga Allah? Kuma mu, a gare Shi, mãsu bautãwa ne.
Say: "Why do you dispute with us about God when He is equally your Lord and our Lord? To us belong our actions, to you yours; and we are true to Him."
Ka ce: Shin kuna jãyayyar hujia ne da mu a cikin al'amarin Allah, alhãli kuwa Shi ne Ubangijinmu kuma Ubangijinku, kuma muna da ayyukanmu, kuma kuna da ayyukanku, kuma mũ, a gare Shi, mãsu tsarkakẽwane?
Or do you claim that Abraham and Ishmael and Isaac and Jacob and their offspring were Jews or Christians? Say: "Have you more knowledge than God?" Who is more wicked than he who conceals the testimony he received from God? God is not unaware of all you do.
Ko kuna cẽwa: Lalle ne, Ibrãhĩm da Ismã'ĩla da Is'hãƙa da Ya'aƙũbu da Jĩkõki, sun kasance Yahũdãwa kõ kuwa Nasãra? Ka ce: Shin kũ ne kuke mafi sani kõAllah? Kuma wãne ne ya zama mafi zãlunci daga wanda ya bõye shaida a wurinsa daga Allah? Kuma Allah bai zama Mai gafala ba daga abin da kuke aikatãwa!
They were the people, and they have passed away. Theirs the reward for what they did, as yours will be for what you do. You will not be questioned about their deeds.
Waccan, wata al'umma ce, tã riga ta shige, suna da abin da suka sana'anta kuma kuna da abin da kuka sana'anta kuma bã a tambayar ku daga abin da suka kasance suna aikatãwa.
The foolish will now ask and say: "What has made the faithful turn away from the Qiblah towards which they used to pray?" Say: "To God belong the East and the West. He guides who so wills to the path that is straight."
Wãwãye daga mutãne zã su ce: Mẽne ne ya jũyar da su daga alƙiblarsu wadda suka kasance a kanta? Ka ce: "Allah ¦ai ne Yake da gabas da yamma, Yana shiryar da wanda Yake so zuwa ga hanya madaidaiciya."
We have made you a temperate people that you act as witness over man, and the Prophet as witness over you. We decreed the Qiblah which you faced before that We may know who follow the Apostle and who turn away in haste. And this was a hard (test) except for those who were guided by God. But God will not suffer your faith to go waste, for God is to men full of mercy and grace.
Kuma kamar wancan, Muka sanya ku al'umma matsakaiciya dõmin ku kasance mãsu bãyar da shaida a kan mutãne. Kuma Manzo ya kasance mai shaida a kanku. Kuma ba Mu sanya Alƙibla wadda ka kasance a kanta ba, fãce dõmin Mu san wanda yake biyar Manzo daga wanda yake jũyãwa a kan duga-dugansa. Kuma lalle ne, tã kasance haƙĩƙa, mai girma, sai a kan waɗanda Allah Ya shiryar. Kuma ba ya yiwuwa ga Allah Ya tõzartar da ĩmãninku. Lalle ne, Allah, ga mutãne, haƙĩƙa, Mai tausayi ne, Mai jin ƙai.
We have seen you turn your face to the heavens. We shall turn you to a Qiblah that will please you. So turn towards the Holy Mosque, and turn towards it wherever you be. And those who are recipients of the Book surely know that this is the truth from their Lord; and God is not negligent of all that you do.
Lalle ne, Muna ganin jujjũyãwar fuskarka a cikin sama. To, lalle ne, Mu jũyar da kai ga Alƙibla wadda kake yardã da ita. Sai ka jũyar da fuskarka wajen Masallãci Tsararre, kuma inda duk kuka kasance, to, ku jũyar da fuskõkinku jiharsa. Kuma lalle ne waɗanda aka bai wa Littãfi, haƙĩƙa su, sunã sanin lalle ne, shĩ ne gaskiya, daga Ubangijinka. Kuma Allah bai zama Mai gafala ba daga abin da suke aikatãwa.
Even though you bring all the proof to the people of the Book they will not face the direction you turn to, nor you theirs, nor will they follow each other's direction. And if you follow their whims after all the knowledge that has reached you, then surely you will be among transgressors.
Kuma hakĩka, idan ka je wawaɗanda aka bai wa Littafi da dukan ãyã, bã zã su bi Alƙiblarka ba, kuma kai ba ka zama mai bin Alƙiblarsu ba, kuma sãshensu bã mai bin Alƙiblar sãshe ba ne. Kuma haƙĩƙa, idan ka bi son zũciyõyinsu daga bãyan abin da ya zo maka daga ilmi, lalle ne kai, sa'an nan, haƙiƙa, azzãlumi kake.
Those to whom We have sent down the Book know this even as they know their sons. Yet a section among them conceals the truth knowingly.
Waɗanda Muka bã su Littãfi, suna saninsa kamar yadda suke sanin ɗiyansu. Kuma lalle ne wani ɓangare daga gare su, haƙiƙa, suna ɓõyewar gaskiya alhãli kuwa sũ, suna sane.
The truth is from your Lord, so be not among those who are sceptics.
Gaskiya daga Ubangijinka take sabõda haka, lalle kada ka kasance daga mãsu shakka.
Each has a goal to which he turns. So strive towards piety and excel the others: God will bring you all together wheresoever you be. God has power over everything.
Kuma kõwane ɓangare yana da alƙibla wadda yake shi mai fuskantar ta ne. Sai ku yi tsẽre zuwa ga ayyukan alhẽri, inda kuka kasance duka Allah zai zo da ku gabã ɗaya. Lalle ne Allah, a kan kõme, Mai ĩkon yi ne.
Wherever you come from turn towards the Holy Mosque: This in truth is from your Lord. God is not negligent of all you do.
Kuma daga inda ka fita, to, sai ka jũyar da fuskarka a wajen Masallãci Tsararre kuma lalle tabbas, shi ne gaskiya daga Ubangijinka. Kuma Allah bai zama Mai gafala ba daga abin da kuke aikatãwa ba.
Whichever place you come from turn towards the Holy Mosque, and wherever you are, turn your faces towards it so that people may have no cause for argument against you, except such among them as are wicked. But do not fear them, fear Me that I may accomplish My favours on you, and you may find the right way perchance.
Kuma daga inda ka fita, to, ka jũyar da fuskarka a wajen Masallãci Tsararre kuma inda kuke duka, to, ku jũyar da fuskõkinku a wajensa, dõmin kada wata hujja ta kasance ga mutãne a kanku, fãce waɗanda suka yi zãlunci daga gare su. Sabõda haka kada ku ji tsõronsu kuma ku ji tsõrõNa kuma dõmin In cika ni'imaTa a kanku, kuma tsammãninku zã ku shiryu.
Even as We sent a messenger from among you to convey Our messages to you and cleanse you, and teach you the Book and the wisdom, and what you did not know;
Kamar yadda Muka aika Manzo a cikinku, daga gare ku, yana karanta ãyõyinMu a gare ku kuma yana tsarkake ku, kuma yana sanar da ku Littãfi da hikima, kuma yana sanar da ku abin da ba ku kasance kuna sani ba.
So, therefore, remember Me, and I shall remember you; and give thanks and do not be ungrateful.
Sabõda haka, ku tuna Ni, In tunã ku, kuma ku yi gõdiya gare Ni, kuma kada ku butulce Mini.
O you who believe, seek courage in fortitude and prayer, for God is with those who are patient and persevere.
Ya ku waɗanda suka yi ĩmãni! Ku nẽmi taimako da haƙuri game da salla. Lalle ne, Allah na tãre da mãsu haƙuri.
Do not say that those who are killed in the way of God, are dead, for indeed they are alive, even though you are not aware.
Kada ku ce ga waɗanda ake kashẽwa a cikin hanyar Allah: "Matattu ne." Ã'a, rãyayyu ne, kuma amma bã ku sansancẽwa.
Be sure We shall try you with something of fear and hunger and loss of wealth and life and the fruits (of your labour); but give tidings of happiness to those who have patience,
Kuma lalle ne, Muna jarrabar ku da wani abu daga tsõro da yunwa da naƙasa daga dũkiya da rãyuka da 'ya'yan itãce. Kuma ka yi bishãra ga mãsu haƙuri.
Who say when assailed by adversity: "Surely we are for God, and to Him we shall return."
Waɗanda suke idan wata masĩfa ta sãme su, sai su ce: "Lalle ne mũ ga Allah muke, kuma lalle ne mũ, zuwa gare Shi, muke kõmãwa."
On such men are the blessings of God and His mercy, for they are indeed on the right path.
Waɗannan akwai albarku a kansu daga Ubangijinsu da wata rahama. Kuma waɗannan sũ ne shiryayyu.
Truly Safa and Marwa are the symbols of God. Whoever goes on pilgrimage to the House (of God), or on a holy visit, is not guilty of wrong if he walk around them; and he who does good of his own accord will find appreciation with God who knows everything.
Lalle ne Safã da Marwa suna daga wurãren ibãdar Allah, to, wanda ya yi hajin ¦ãki kõ kuwa ya yi Umra, to, bãbu laifi a kansa ga ya yi ɗawãfi gare su, su biyu. Kuma wanda ya ƙãra yin wani aikin alhẽri to, lalle ne Allah Mai gõdiya ne, Masani.
They who conceal Our signs and the guidance We have sent them and have made clear in the Book, are condemned of God and are condemned by those who are worthy of condemning.
Lalle ne waɗanda suke ɓõyẽwar abin da Allah Ya saukar da ga hujjõji bayyanannu, da shiriya, daga bãyan Mun bayyana shi ga mutãne, a cikin Littãfi (Alƙur'ãni), waɗannan Allah Yana la'anar su, kuma mãsu la'ana suna la'anar su.
But those who repent and reform and proclaim (the truth), are forgiven, for I am forgiving and merciful.
Sai waɗanda suka tũba, kuma suka gyãra, kuma suka bayyana, to waɗannan Ina karɓar tũba a kansu kuma Nĩ ne Mai karɓar tũba, Mai jin ƙai.
But those who deny, and die disbelieving, bear the condemnation of God and the angels and that of all men,
Lalle ne, waɗanda suka kãfirta kuma suka mutu alhãli kuwa suna kãfirai, waɗannan akwai, a kansu, la'anar Allah da Malã'iku da mutãne gabã ɗaya.
Under which they will live, and their suffering will neither decrease nor be respite for them.
Suna madawwama a cikinta, bã a sauƙaƙa azãba daga barinsu, kuma ba su zama ana jinkirta musu ba.
Your God is one God; there is no god other than He, the compassionate, ever-merciful.
Kuma Ubangijinku Ubangiji Guda ne. Bãbu wani Ubangiji fãce Shi, Mai rahama, Mai jin ƙai.
Creation of the heavens and the earth, alternation of night and day, and sailing of ships across the ocean with what is useful to man, and the rain that God sends from the sky enlivening the earth that was dead, and the scattering of beasts of all kinds upon it, and the changing of the winds, and the clouds which remain obedient between earth and sky, are surely signs for the wise.
Lalle ne, a cikin halittar sammai da ƙasa, da sãɓãwar dare da yini, da jirãge wadaɗnda suke gudana a cikin tẽku (ɗauke) da abin da yake amfãnin mutãne, da abin da Allah Ya saukar daga sama daga ruwa, sai Ya rãyar da ƙasa da shi a bãyan mutuwarta, kuma Ya wãtsa, a cikinta, daga dukan dabba, kuma da jũyãwar iskõki da girgije hõrarre a tsakãnin sama da ƙasa; haƙĩƙa, akwaiãyõyi ga mutãne mãsu yin hankali.
And yet there are men who take others as compeers of God, and bestow on them love due to God; but the love of the faithful for God is more intense. If only the wicked could see now the agony that they will behold (on the Day of Resurrection), they will know that to God belongs the power entirely'. And the punishment of God is severe.
Kuma akwai daga mutãne wanda yake riƙon kinãye, baicin Allah, suna son su, kamar son Allah, kuma waɗanda suka yi ĩmãni ne mafiya tsananin so ga Allah. Kuma dã waɗanda suka yi zãlunci, suna ganin lõkacin da zã su ga azãba, da cewa lalle ne ƙarfi ga Allah yake duka, da cẽwa lalle neAllah Mai tsananin azãba ne.
When those who were followed will disclaim those who followed them, and see the torment all ties between them shall be severed,
A lõkacin da waɗanda aka bi suka barranta daga waɗanda suka bi, kuma suka ga azãba, kuma sabubba suka yanke da su.
And the followers will say: "Could we live but once again we would leave them as they have abandoned us now." God will show them thus their deeds, and fill them with remorse; but never shall they find release from the Fire.
Kuma waɗanda suka bi, suka ce: "Dã lalle ne muna da wata kõmãwa (dũniya) sai mu barranta dagagare su kamar yadda suka barranta daga gare mu (dã ba su riƙi kinãyen ba)." Kamar wancan ne Allah ke nũna musu ayyukansu, suna da nadãmõmi a kansu, kuma ba su zama mãsu fita daga wutar ba.
O men, eat only the things of the earth that are lawful and good. Do not walk in the footsteps of Satan, your acknowledged enemy.
Yã ku mutãne! Ku ci daga abin da yake a cikin ƙasa, wanda yake halal, mai dãɗi. Kuma kada ku bi zambiyõyin Shaiɗan. Lalle ne shi, gare ku, maƙiyi ne bayyananne.
He will ask you to indulge in evil, indecency, and to speak lies of God you cannot even conceive.
Yana umurnin ku ne kawai da mugun aiki da alfãsha, kuma da ku faɗi abin da ba ku sani ba ga Allah.
When it is said to them: "Follow what God has revealed," they reply: "No, we shall follow only what our fathers had practiced," -- even though their fathers had no wisdom or guidance!
Kuma idan aka ce musu: "Ku bi abin da Allah Ya saukar," sai su ce: Ã'a, muna bin abin da muka iske ubanninmu a kansa." Shin, kuma kõ dã ubanninsu bã su hankaltar kõme, kuma bã su shiryuwa?
The semblance of the infidels is that of a man who shouts to one that cannot hear more than a call and a cry. They are deaf, dumb and blind, and they fail to understand.
Kuma misãlin (mai kiran) waɗanda suka kãfirta kamar misãlin wanda ke yin me! me! ga abin da ba ya ji ne, fãce kira da ƙãra, kurãme, bẽbãye, makafi, sabõda haka bã su hankalta.
O believers, eat what is good of the food We have given you, and be grateful to God, if indeed you are obedient to Him.
Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Ku ci ku sha daga mãsu dãɗin abin da Muka azurta ku. Kuma ku gõde wa Allah, idan kun kasance Shi kuke bauta wa.
Forbidden to you are carrion and blood, and the flesh of the swine, and that which has been consecrated (or killed) in the name of any other than God. If one is obliged by necessity to eat it without intending to transgress, or reverting to it, he is not guilty of sin; for God is forgiving and kind.
Kawai abin da Ya haramta a kanku, mũshe da Jini da nãman alade da abin da aka kurũrũta game da shi ga wanin Allah. To, wanda aka matsã, wanin ɗan tãwãye, kuma banda mai zãlunci, to bãbu laifi a kansa. Lalle ne Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai.
Those who conceal any part of the Scriptures that God has revealed, and thus make a little profit thereby, take nothing but fire as food; and God will not turn to them on the Day of Resurrection, nor nourish them for growth; and their doom will be painful.
Lalle ne waɗannan da suke ɓõye abin da Allah Ya saukar daga Littãfi, kuma suna sayen kuɗi kaɗan da shi; waɗannan bã su cin kome a cikin cikkunansu fãce wuta, kuma Allah bã zai yi musu magana ba a Rãnar ¡iyãma, kuma bã zai tsarkake su ba, kuma suna da azãba mai raɗaɗi.
They are those who bartered away good guidance for error, and pardon for punishment: How great is their striving for the Fire
Waɗannan su ne waɗanda suka sayi ɓata da shiriya, kuma azãba da gãfara. To, me ya yi haƙurinsu a kan Wuta!
That is because God has revealed the Book containing the truth; but those who are at variance about it have gone astray in their contrariness.
Wancan dõmin lalle ne Allah Ya saukar da Littafi da gaskiya, kuma lalle ne waɗanda suka sãɓã a cikin Littãfin, haƙĩƙa, suna a cikin sãɓãni mai nĩsa.
Piety does not lie in turning your face to East or West: Piety lies in believing in God, the Last Day and the angels, the Scriptures and the prophets, and disbursing your wealth out of love for God among your kin and the orphans, the wayfarers and mendicants, freeing the slaves, observing your devotional obligations, and in paying the zakat and fulfilling a pledge you have given, and being patient in hardship, adversity, and times of peril. These are the men who affirm the truth, and they are those who follow the straight path.
Bai zama addini ba dõmin kun jũyar da fuskõkinku wajen gabas da yamma, kuma amma addini shi ne ga wanda ya yi ĩmãni da Allah da Rãnar Lãhira da malã'iku da Littattafan sama da Annabãwa, kuma ya bãyar da dũkiya, akan yana son ta, ga mai zumunta da marãyu da matalauta da ɗan hanya da mãsu rõƙo, kuma a cikin fansar wuya, kuma ya tsayar da salla, kuma ya bãyar da zakka, da mãsu cika alkawari idan sun ƙulla alkawarin da mãsu haƙuri a cikin tsanani da cũta da lõkacin yãƙi. Waɗannan su ne suka yi gaskiya. Kuma waɗannan su ne mãsu taƙawa.
O believers, ordained for you is retribution for the murdered, (whether) a free man (is guilty) of (the murder of) a free man, or a slave of a slave, or a woman of a woman. But he who is pardoned some of it by his brother should be dealt with equity, and recompense (for blood) paid with a grace. This is a concession from your Lord and a kindness. He who transgresses in spite of it shall suffer painful punishment.
Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! An wajabta, a kanku, yin ƙisãsi a cikin kasassu. ɗa da ɗa kuma bãwa da bãwa, kuma mace da mace, to, wanda aka yi rangwamen wani abu gare shi daga ɗan'uwansa to a bi da alhẽri da biya zuwa gare, shi da kyautatãwa. Wancan sauƙaƙewa ne daga Ubangijinku, kuma rahama ce. To, wanda ya yi zãlunci a bãyan wancan, to, yana da azãba mai raɗaɗi.
In retribution there is life (and preservation). O men of sense, you may haply take heed for yourselves.
Kuma kuna da rãyuwa a cikin ƙisãsi, yã ma'abuta hankula; tsammãninku, zã ku yi taƙawa.
It is ordained that when any one of you nears death, and he owns goods and chattels, he should bequeath them equitably to his parents and next of kin. This is binding on those who are upright and fear God.
Kuma an wajabta, a kanku idan mutuwa ta halarci ɗayanku, idan ya bar wata dũkiya, wasiyya dõmin mahaifa da dangi bisa ga abin da aka sani; wajabce a kan mãsu taƙawa.
And any one who changes the will, having heard it, shall be guilty and accountable; for God hears all and knows everything.
To, wanda ya musanya masa a bãyan ya ji shi, to, kawai laifinsa yana a kan waɗanda suke musanya shi. Lalle ne, Allah Mai ji ne, Masani.
He who suspects wrong or partiality on the part of the testator and brings about a settlement, does not incure any guilt, for God is verily forgiving and merciful.
To, wanda ya ji tsõron karkata ko kuwa wani zunubi daga mai wasiyyar, sai ya yi sulhi a tsakãninsu to bãbu laifi a kansa. Lalle ne Allah, Mai gãfara ne, Mai jin ƙai.
O believers, fasting is enjoined on you as it was on those before you, so that you might become righteous.
Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! An wajabta azumi a kanku kamar yadda aka wajabta shi a kan waɗanda suke daga gabãninku, tsammãninku, zã ku yi taƙawa,
Fast a (fixed) number of days, but if someone is ill or is travelling (he should complete) the number of days (he had missed); and those who find it hard to fast should expiate by feeding a poor person. For the good they do with a little hardship is better for men. And if you fast it is good for you, if you knew.
Kwanuka ƙidãyayyu. To, wanda ya kasance daga gare ku majinyaci ko kuwa yana a kan tafiya, sai (ya biya) adadi daga wasu kwanuka na dabam. Kuma a kan waɗanda suke yin sa da wahala akwai fansa; ciyar da matalauci, sai dai wanda ya ƙãra alhẽri to, shi ne mafi alhẽri a gare shi. Kuma ku yi azumi (da wahalar) ne mafi alhẽri a gare ku idan kun kasance kuna sani.
Ramadan is the month in which the Qur'an was revealed as guidance to man and clear proof of the guidance, and criterion (of falsehood and truth). So when you see the new moon you should fast the whole month; but a person who is ill or travelling (and fails to do so) should fast on other days, as God wishes ease and not hardship for you, so that you complete the (fixed) number (of fasts), and give glory to God for the guidance, and be grateful.
Watan Ramalãna ne wanda aka saukar da Alƙur'ãni a cikinsa yana shiriya ga mutãne da hujjõji bayyanannu daga shiriya da rarrabẽwa. To, wanda ya halarta daga gare ku a watan, sai ya azumce shi, kuma wanda ya kasance majinyaci ko kuwa a kan tafiya, sai ya biya adadi daga wasu kwanuka na dabam. Allah Yana nufin sauƙi gare ku, kuma ba Ya nufin tsanani gare ku, kuma dõmin ku cika adadin, kuma dõmin ku girmama Allah a kan Yã shiryar da ku, kuma tsammãninku, zã ku gõde.
When My devotees enquire of you about Me, I am near, and answer the call of every supplicant when he calls. It behoves them to hearken to Me and believe in Me that they may follow the right path.
Kuma idan bãyiNa suka tambaye ka daga gare Ni, to, lalle Ni Makusanci ne. Ina karɓa kiran mai kira idan ya kirã Ni. Sabõda haka su nẽmi karɓawaTa, kuma su yi ĩmãni da Ni: tsammãninsu, su shiryu.
You are allowed to sleep with your wives on the nights of the fast: They are your dress as you are theirs. God is aware you were cheating yourselves, so He turned to you and pardoned you. So now you may have intercourse with them, and seek what God has ordained for you. Eat and drink until the white thread of dawn appears clear from the dark line, then fast until the night falls; and abstain from your wives (when you have decided) to stay in the mosques for assiduous devotion. These are the bounds fixed by God, so keep well within them. So does God make His signs clear to men that they may take heed for themselves.
An halatta a gare ku, a daren azumi, yin jima'i zuwa ga matanku sũ tufa ne a gare ku, kuma kũ tufa ne a gare su, Allah Yã sani lalle ne ku kun kasance kuna yaudarar kanku. Sabõda haka Yã karɓi tũbarku, kuma Yã yãfe muku. To, yanzu ku rungume su kuma ku nẽmi abin da Allah yã rubũta muku. Kuma ku ci kuma ku sha har sĩlĩli fari ya bayyana a gare ku daga sĩlĩli baƙi daga alfijiri, sa'an nan kuma ku cika azumi zuwa ga dare. Kuma kada ku rungume su alhãli kuna mãsu itikãfi a cikin masallãtai. Waɗancan iyãkokin Allah ne: don haka kada ku kusancesu kamar haka ne Allah Yake bayyana ãyõyinSa ga mutãne: tsammãninsu, zã su yi taƙawa.
And do not consume each other's wealth in vain, nor offer it to men in authority with intent of usurping unlawfully and knowingly a part of the wealth of others.
Kada ku ci dukiyõyinku a tsakãninku da ƙarya, kuma ku sãdu da ita zuwa ga mahukunta dõmin ku ci wani yanki daga dũkiyõyin mutãne da zunubi alhãli kuwa kũ, kuna sane.
They ask you of the new moons. Say: "These are periods set for men (to reckon) time, and for pilgrimage." Piety does not lie in entering the house through the back door, for the pious man is he who follows the straight path. Enter the house through the main gate, and obey God. You may haply find success.
Kuma suna tambayar ka daga jirajiran wata. Ka ce: "Su lõkatai ne dõmin mutãne da haji, kuma bã addini ba ne ku je wa gidãje daga bãyansu: kuma amma abin da yake addini shi ne wanda ya yi taƙawa. Kuma ku je wa gidãje daga ƙõfõfinsu, kuma ku bi Allah da taƙawa: tsammãninku, ku ci nasara.
Fight those in the way of God who fight you, but do not be aggressive: God does not like aggressors.
Kuma ku yãƙi waɗanda suke yãƙinku, a cikin hanyar Allah, kuma kada ku yi tsõkana, lalle ne Allah bã Ya son mãsu tsõkana.
And fight those (who fight you) wheresoever you find them, and expel them from the place they had turned you out from. Oppression is worse than killing. Do not fight them by the Holy Mosque unless they fight you there. If they do, then slay them: Such is the requital for unbelievers.
Kuma ku yãƙe su inda kuka sãme su, kuma ku fitar da su daga inda suka fitar da ku. Kuma fitina ita ce mafi tsanani daga kisa. Kuma kada ku yãƙe su a wurin Masallãci Tsararre (Hurumin Makka) fãce fa idan sun yãƙe ku a cikinsa. To, idan sun yãƙe ku, sai ku yãƙe su. Kamar wancan ne sakamakon kãfirai yake.
But if they desist, God is forgiving and kind.
Sa'an nan idan sun hanu, to, lalle Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai.
Fight them till sedition comes to end, and the law of God (prevails). If they desist, then cease to be hostile, except against those who oppress.
Kuma ku yãƙe su har ya zama wata fitina bã zã ta kasance ba, kuma addini ya zama na Allah. Sa'an nan idan sun hanu to bãbu tsõkana fãce a kan azzãlumai.