english
stringlengths
4
2.18k
hausa
stringlengths
3
1.38k
In the name of Allah, most benevolent, ever-merciful.
Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.
ALL PRAISE BE to Allah, Lord of all the worlds,
Godiya ta tabbata ga Allah, Ubangijin halittu;
Most beneficent, ever-merciful,
Mai rahama, Mai jin ƙai;
King of the Day of Judgement.
Mai nuna Mulkin Rãnar Sakamako.
You alone we worship, and to You alone turn for help.
Kai muke bauta wa, kuma Kai muke neman taimakonKa.
Guide us (O Lord) to the path that is straight,
Ka shiryar da mu ga hanya madaidaiciya.
The path of those You have blessed, Not of those who have earned Your anger, nor those who have gone astray.
Hanyar waɗanda Ka yi wa ni'ima, ba waɗanda aka yi wa fushi ba, kuma ba ɓatattu ba.
ALIF LAM MIM.
A. L̃. M̃.
This is The Book free of doubt and involution, a guidance for those who preserve themselves from evil and follow the straight path,
Wãncan ne Littãfi, bãbu shakka a cikinsa, shiriya ne ga mãsu taƙawa.
Who believe in the Unknown and fulfil their devotional obligations, and spend in charity of what We have given them;
Waɗanda suke yin ĩmãni game da gaibi, kuma suna tsayar da salla, kuma daga abin da Muka azurta su suna ciyarwa.
Who believe in what has been revealed to you and what was revealed to those before you, and are certain of the Hereafter.
Kuma waɗanda suke yin ĩmãni da abin da aka saukar zuwa gare ka, da abin da aka saukar daga gabãninka, kuma game da Lãhira suna yin yaƙĩni.
They have found the guidance of their Lord and will be successful.
Waɗannan suna kan shiriya, daga Ubangjinsu, kuma waɗannan su ne mãsu cin nasara.
As for those who deny, it is all the same if you warn them or not, they will not believe.
Lalle ne waɗanda suka kãfirta daidai ne a kansu, shin kã yi musu gargaɗi kõ ba ka yi musu gargaɗi ba, ba zã su yi ĩmãni ba.
God has sealed their hearts and ears, and veiled their eyes. For them is great deprivation.
Allah Ya sa hãtimi a kan zukãtansu, da a kan jinsu, kuma a Kan ganin su akwai wata yãna; kuma suna da wata azãba mai girma.
And there are some who, though they say: "We believe in God and the Last Day," (in reality) do not believe.
Kuma akwai daga mutãne wanda yake cewa: "Mun yi imani da Allah kuma da Yinin Lãhira." Alhãli kuwa su ba muminai ba ne.
They (try to) deceive God and those who believe, yet deceive none but themselves although they do not know.
Suna yaudarayya da Allah da waɗanda suka yi ĩmãni, alhãli bã su yaudarar kõwa fãce kansu, kuma bã su sakankancẽwa!
Sick are their hearts, and God adds to their malady. For them is suffering for they lie.
A cikin zukãtansu akwai wata cũta. Sai Allah Ya ƙãramusu wata cũta, kuma suna da azãba mai raɗaɗi sabõda ãbin da suka kasance suna yi na ƙarya.
When asked to desist from spreading corruption in the land they say: "Why, we are reformers."
Kuma idan aka ce musu: "Kada ku yi ɓarna a cikin ƙasa," sukan ce: "Mũ mãsu kyautatawa kawai ne!"
Yet they are surely mischief-mongers, even though they do not know.
To, lalle ne su, sũne mãsu ɓarna, kuma amma bã su sansancewa.
When asked to believe as others do, they say: "Should we believe like fools?" And yet they are the fools, even though they do not know.
Kuma idan aka ce musu: "ku yi ĩmãni kamar yadda mutãne suka yi ĩmãni," sukan ce: "Zã mu yi ĩmãni ne kamar yadda wãwãye suka yi ĩmãni?" To, lalle ne su, sũ ne wãwãye, kuma amma bã su sani.
When they meet the faithful they say: "We believe;" but when alone with the devils (their fellows), they say: "We are really with you; we were joking."
Kuma idan sun haɗu da waɗanda suka yi ĩmãni, sukan ce: "Mun yi ĩmãni. "Kuma idan sun wõfinta zuwa ga shaiɗãnunsu, sukan ce: "Lalle ne muna tãre da ku: Mu mãsu izgili, kawai ne."
But God will turn the joke against them and allow them to sink deeper into evil and wander perplexed in their wickedness.
Allah Yana yin izgili gare su kuma Yana taimakon su a cikin ɓatarsu, suna ɗimuwa.
They are indeed those who bartered away good guidance for error and gained nothing from the deal, nor found the right way.
Waɗannan su ne waɗanda suka sayi ɓata da shiriya, sai fataucinsu bai yi rĩba ba, kuma ba su kasance masu shiryuwa ba.
They are like a man who kindles a fire, and when its glow has illumined the air God takes away their light leaving them in the dark where they will not be able to see.
Misãlinsu shĩ ne kamar misãlin wanda ya hũra wuta, to, a lõkacin da ta haskake abin da yake gẽfensa (na abin tsõro), Allah Ya tafi da haskensu, kuma Ya bar su a cikin duffai, bã su gani.
They are deaf, dumb and blind, and shall never return;
Kurãme, bẽbãye, makãfi, sabõda haka bã su kõmõwa.
Or like rain pouring from the sky which hides within it darkness, thunder and lightning. They thrust their fingers into their ears for safety against noise and death. But God surrounds those who believe not from all sides.
Ko kuwa kamar girgije mai zuba daga sama, a cikinsa akwai duffai da tsãwa da walƙiya: suna sanyãwar yãtsunsu a cikin kunnuwansu dãga tsãwarwakin, dõmin tsõron mutuwa. Kuma Allah Mai kẽwayewane gã kãfirai!
Verily the lightning could snatch away their eyes. When it flashes forth they walk in its flare. When darkness returns they stand still. And if the Lord wills so He could take away their hearing and sight; surely God is all-powerful.
Walƙiyar tana yin kusa ta fizge gannansu, ko da yaushe ta haskakã musu, sai su yi tafiya a cikinta, kuma idan ta yi duhu a kansu, sai su yi tsaye. Kuma dã Allah Yã so, sai Ya tafi da jinsu da gannansu. Lalle ne Allah a kan dukan kõme Mai ĩkon yi ne.
So, O you people, adore your Lord who created you, as He did those before you, that you could take heed for yourselves and fear Him
Yã ku mutãne! Ku bauta wa Ubangjinku, Wanda Ya halicce ku, kũ da waɗanda suke daga gabãninku, tsammãninku ku kãre kanku!
Who made the earth a bed for you, the sky a canopy, and sends forth rain from the skies that fruits may grow -- your food and sustenance. So, do not make another the equal of God knowingly.
Wanda Ya sanya muku ƙasa shimfiɗa, kuma sama gini, kuma Ya saukar da ruwa daga sama, sa'an nan Ya fitar da abinci daga 'ya'yan itãce game da shi, sabõda ku. Sabõda haka kada ku sanya wa Allah wasu kĩshiyõyi, alhãli kuwa kuna sane.
If you are in doubt of what We have revealed to Our votary, then bring a Surah like this, and call any witness, apart from God, you like, if you are truthful.
Kuma idan kun kasance a cikin shakka daga abin da Muka sassaukar ga Bãwanmu, to, ku zõ da sũra guda daga misalinsa (Alƙur'ãni). Kuma ku kirãwo shaidunku baicin Allah, idan kun kasance mãsu gaskiya.
But if you cannot, as indeed you cannot, then guard yourselves against the Fire whose fuel is men and rocks, which has been prepared for the infidels.
To, idan ba ku aikata (kãwo sura) ba, to, bã zã ku aikataba, sabõda haka, ku ji tsoron wuta, wadda makãmashinta mutãne da duwãtsu ne, an yi tattalinta dõmin kãfurai.
Announce to those who believe and have done good deeds, glad tidings of gardens under which rivers flow, and where, when they eat the fruits that grow, they will say: "Indeed they are the same as we were given before," so like in semblance the food would be. And they shall have fair spouses there, and live there abidingly.
Kuma ka bãyar da bishãra ga waɗanda suka yi ĩmãni. kuma suka aikata ayyuka na ƙwarai, cẽwa lallene, suna da gidãjen Aljanna, ƙõramu na gudãna daga ƙarƙashinsu. Ko da yaushe aka azurta su da abinci daga wasu 'ya'yan itãce daga gare su, sai su ce: "Wannan shi ne aka azurta mu da shi daga gabãnin haka," Kuma a je musu da shi yana mai kama da juna, Kuma sunã da, a cikin su, mãtan aure mãsu tsarki, kuma su, cikin su madawwama ne.
God is not loath to advance the similitude of a gnat or a being more contemptible; and those who believe know whatever is from the Lord is true. But those who disbelieve say: "What does God mean by this parable?" He causes some to err this way, and some He guides; yet He turns away none but those who transgress,
Lalle ne, Allah bã Ya jin kunyar Ya bayyana wani misãli, kõwane iri ne, sauro da abin da yake bisa gare shi. To, amma waɗanda suka yi ĩmãni, sai su san cewa lalle shi ne gaskiya daga Ubangijin su, kuma amma waɗanda suka kãfirta, sai su ce: "Mẽne ne Allah Ya yi nufi da wannan ya zama misãli?" na ɓatar da wasu mãsu yawa da shi, kuma Yana shiryar da wasu mãsu yawada shi, kuma bã Ya ɓatarwa da shi fãce fasiƙai.
Who, having sealed it, break God's covenant, dividing what He ordained cohered; and those who spread discord in the land will suffer assuredly.
Waɗanda suke warware alƙawarin Allah daga bãyan ƙulla shi, kuma su yanke abin da Allah Ya yi umurni da shi a sãdar, kuma suna ɓarna a cikin ƙasa, waɗannan sũ ne mãsu hasãra.
Then how can you disbelieve in God? He gave you life when you were dead. He will make you die again then bring you back to life: To Him then you will return.
Yaya kuke kãfirta da Allah, alhãli kuwa kun kasance matattu sa'an nan Ya rãyar da ku, sa'nnan kuma Ya matar da ku, sa'an nan kuma Ya rãya ku, sa'an nan zuwa gare Shi ake mayar da ku?
He made for you all that lies within the earth, then turning to the firmament He proportioned several skies: He has knowledge of everything.
Shi ne Wanda Ya halitta muku abin da ke a cikin ƙasa gaba ɗaya, sa'an nan kuma Ya daidaita zuwa sama, sa'an nan Y a aikata su sammai bakwai. Kuma Shi ga dukan kõmai Masani ne.
Remember, when your Lord said to the angels: "I have to place a trustee on the earth," they said: "Will You place one there who would create disorder and shed blood, while we intone Your litanies and sanctify Your name?" And God said: "I know what you do not know."
Kuma a lõkacin da Ubangijinka Ya ce ga malã'iku: "Lalle ne, Ni Mai sanya wani halĩfa ne a cikin ƙasa," suka ce: "Ashe, zã Ka sanya a cikinta, wanda zai yi ɓarna a cikinta, kuma mu, muna yi maka tasbihi tare da gõde maka, kuma muna tsarkakewa gareka" Ya ce: "Lalle ne, Ni Na san abin da ba ku sani ba."
Then He gave Adam knowledge of the nature and reality of all things and everything, and set them before the angels and said: "Tell Me the names of these if you are truthful."
Kuma Ya sanar da Ãdam sũnãye dukansu, sa'an nan kuma ya gitta su a kan malã'iku, sa'n nan Ya ce: "Ku gaya mini sũnayen waɗannan, idan kun nasance mãsu gaskiya."
And they said: "Glory to You (O Lord), knowledge we have none except what You have given us, for You are all-knowing and all-wise."
Suka ce: "Tsarki ya tabbata a gare Ka! Bãbu sani a gare mu, lalle ne Kai, Kai ne Masani, Mai hikima."
Then He said to Adam: "Convey to them their names." And when he had told them, God said: "Did I not tell you that I know the unknown of the heavens and the earth, and I know what you disclose and know what you hide?"
Ya ce: "Yã Ãdam! Ka gaya musu sũnãyensu." To, a lokacin da ya gaya musu sũnãyensu, (Allah) Ya ce: "Ashe, ban ce muku ba, lalle Ni, Inã sane da gaibin sammai da ƙasa, kuma (Inã sane da) abin da kuke bayyanawa da abin da kuka kasance kuna ɓõyewa?"
Remember, when We asked the angels to bow in homage to Adam, they all bowed but Iblis, who disdained and turned insolent, and so became a disbeliever.
Kuma a lõkacin da Muka ce ga malã'iku: "Ku yi sujada ga Ãdam," Sai suka yi sujada, fãce Ibilĩsa ya ƙi, kuma ya yi girman kai, kuma ya kasance daga kãfirai.
And We said to Adam: "Both you and your spouse live in the Garden, eat freely to your fill wherever you like, but approach not this tree or you will become transgressors.
Kuma muka ce: "Ya Ãdam! Ka zauna kai da matarka a gidan Aljanna, kuma ku ci daga gare ta, bisa wadãta, inda kuke so, kuma kada ku kusanci wannan itãciyar, har ku kasance daga azzãlumai."
But Satan tempted them and had them banished from the (happy) state they were in. And We said: "Go, one the antagonist of the other, and live on the earth for a time ordained, and fend for yourselves."
Sai Shaiɗan ya talãlãɓantar da su ga barinta, sai ya fitar da su daga abin da suka kasance a cikinsa. Kuma muka ce: "Sãshenku nã maƙiyi ga sãshe, kuma kuna da a cikin ƙasa matabbata da jin dãɗi zuwa ga wani lõkaci."
Then his Lord sent commands to Adam and turned towards him: Indeed He is compassionate and kind.
Sai Ãdam ya karɓi wasu kalmõmi daga Ubangjjinsa, sabõda haka ya karɓi tũba a kansa. Lalle ne Shi, Shĩ ne Mai karɓar tũba, Mai jin ƙai.
And We said to them: "Go, all of you. When I send guidance, whoever follows it will neither have fear nor regret;
Muka ce: "Ku ku sauka daga gare ta gabã ɗaya. To, imma lalle shiriya ta je muku daga gare Ni, to, wanda ya bi shiriya ta to, bãbu tsõro a kansu, kuma bã su yin baƙin ciki."
But those who deny and reject Our signs will belong to Hell, and there abide unchanged."
"Kuma waɗanda suka kãfirta, kuma suka ƙaryata game da ãyõyinMu, waɗannan sũ ne abõkan Wuta; sũ a cikinta madawwama ne."
O children of Israel, remember the favours I bestowed on you. So keep your pledge to Me, and I will mine to you, and be fearful of Me,
Yã Banĩ Isrã'Ĩla! Ku tuna ni'imãTa a kanku, kuma ku cika alƙawariNa, In cika muku da alƙawarinku. kuma Ni, ku ji tsõro Na.
And believe in what I have sent down which verifies what is already with you; and do not be the first to deny it, nor part with it for little gain; and beware of Me.
Kuma, ku yi ĩmãni da abin da na saukar, mai gaskatãwa ga abin da yake tãre da ku, kuma kada ku kasance farkon kãfiri game da shi, Kuma kada ku sayi 'yan kuɗi kaɗan da ãyõyiNa. Kuma ku ji tsõrõNa, Nĩ kaɗai.
Do not confuse truth with falsehood, nor conceal the truth knowingly.
Kuma kada ku lulluɓe gaskiya da ƙarya, kuma ku ɓõye gaskiya, alhãli kuwa kuna sane.
Be firm in devotion; give zakat (the due share of your wealth for the welfare of others), and bow with those who bow (before God).
Kuma ku tsayar da salla; kuma ku bãyar da zakka; kuma ku yi rukũ'i tãre da mãsu yin rukũ'i.
Will you enjoin good deeds on the others and forget your own selves? You also read the Scriptures, why do you then not understand?
Shin, kuna umurnin mutãne da alhẽri, kuma ku manta da kanku alhãli kuwa kuna karatun littãfi? Shin, bãzã ku hankalta ba?
Find strength in fortitude and prayer, which is heavy and exacting but for those who are humble and meek,
Kuma ku nẽmi taimako da yin haƙuri, da salla. Kuma lalle ne ita, haƙĩƙa, mai girma ce fãce fa a kan mãsu tsõron Allah.
Who are conscious that they have to meet their Lord, and to Him they have to return.
Waɗanda suka tabbata cẽwa lalle ne su mãsu haɗuwa da Ubangijinsu, kuma lalle ne sũ a gareshi mãsu kõmãwa ne.
Remember, O children of Israel, the favours I bestowed on you, and made you exalted among the nations of the world.
Yã banĩ Isrã'ĩla! Ku tuna ni'imaTa, wadda Na ni'imta a kanku, kuma lalle ne Ni, na fĩfĩta ku a kan tãlikai.
Take heed of the day when no man will be useful to man in the least, when no intercession matter nor ransom avail, nor help reach them.
Kuma ku ji tsron wani yini, (a cikinsa) rai bã ya Wadãtar da wani rai da kõme, kuma bã a karɓar cetõ daga gareshi, kuma ba a karɓar fansa daga gare shi, kuma bã su zama ana taimakon su ba.
Remember, We saved you from the Pharaoh's people who wronged and oppressed you and slew your sons but spared your women: In this was a great favour from your Lord.
Kuma a lõkacin da muka tsĩrar da ku daga mutãnen Fir'auna, su na taya muku muguntar azãba, su na yayyanke ɗiyanku maza su na rãyar da mãtanku. Kuma a cikin wancan akwai jarabawa mai girma daga Ubangijinku.
Remember, We parted the sea and saved you, and drowned the men of Pharaoh before your very eyes.
Kuma a lõkacin da Muka raba tẽku sabõda ku, sai Muka tsĩrar da ku kuma Muka nutsar da mutãnen Fir'auna, alhãli kuwa kũ kuna kallo.
Yet, remember, as We communed with Moses for forty nights you took the calf in his absence (and worshipped it), and you did wrong.
Kuma a lõkacin da muka yi wa'adi ga Mũsa, dare arba'in, sa'an nan kuma kuka riƙi maraƙi daga bãyansa, alhãli kũ, kuna mãsu zãlunci (da bauta masa).
Even so, We pardoned you that you may be grateful.
Sa'an nan kuma muka yãfe muku daga bãyan wancan, tsammãninku, kuna gõdẽwa.
Remember, We gave Moses the Book and Discernment of falsehood and truth, that you may be guided.
Kuma a lõkacin da Muka baiwa Mũsa Littãfi da rarrabẽwa, tsammãninku, kuna shiryuwa.
Remember, Moses said: "My people, by taking this calf you have done yourselves harm, so now turn to your Creator in repentance, and kill your pride, which is better with your Lord." And (the Lord) softened towards you, for He is all-forgiving and merciful.
Kuma a lõkacin da Mũsa ya ce ga mutãnensa: "Ya mutãnena! Lalle ne ku, kun zãlunci kanku game da riƙonku maraƙin, sai ku tũba zuwa ga Mahaliccinku, sai ku kashe kãwunanku. Wancan ne mafii alheri a wajen mahaliccinku. Sa'an nan Ya karɓi tuba a kanku. lalle ne Shi, Shi ne Mai karɓar tũba, Mai jin ƙai.
Remember, when you said to Moses: "We shall not believe in you until we see God face to face," lightning struck you as you looked.
Kuma a lõkacin da kuka ce: "Ya Musa! Bã zã mu yi ĩmãni ba dõminka, sai munga Allah bayyane," sabada haka tsãwar nan ta kamaku, alhãli kuwa kuna kallo.
Even then We revived you after you had become senseless that you might give thanks;
Sa'an nan kuma Muka tãyar da ku daga bãyan mutuwarku, tsammãninku, kuna gõdẽwa.
And made the cloud spread shade over you, and sent for you manna and quails that you may eat of the good things We have made for you. No harm was done to Us, they only harmed themselves.
Kuma Muka sanya girgije ya yi inuwa a kanku, kuma Muka saukar da darɓa da tantabaru a kanku; "Ku ci daga mãsu dãɗin abin da Muka azurta ku." kuma ba su zãlunce Mu ba, kuma amma kansu suka kasance suna zãlunta.
And remember, We said to you: "Enter this city, eat wherever you like, as much as you please, but pass through the gates in humility and say: 'May our sins be forgiven.' We shall forgive your trespasses and give those who do good abundance.
Kuma a lokacin da Muka ce: "Ku shiga wannan alƙarya. San nan ku ci daga gareta, idan kuka so, bisa wadata, kuma ku shiga ƙofa kuna masu tawalu'i, kuma ku ce; "kãyar da zunubai" Mu gãfarta muku laifukanku, kuma zã mu ƙãra wa mãsu kyautatawa."
But the wicked changed and perverted the word We had spoken to a word distorted, and We sent from heaven retribution on the wicked, for they disobeyed.
Sai waɗanda suka yi zalunci suka sake magana watar wannan da aka ce musu, saboda haka muka saukar a kan waɗanda suka yi zãlunci da azãba daga sama sabõda abin da suka kasance suna yi na fãsiƙanci.
And remember, when Moses asked for water for his people, We told him to strike the rock with his staff, and behold, twelve springs of gushing water gushed forth so that each of the tribes came to know its place of drinking. Eat and drink, (enjoy) God's gifts, and spread no discord in the land.
Kuma a lokacin da Mũsa ya nemi shãyarwa domin mutãnensa, Muka ce; "Ka dõki dũtsen da sandarka." Sai marmaro gõma sha biyu suka ɓuɓɓugo, haƙĩƙa, kõwaɗanne mutãne sun san wurin shansu. "Ku ci kuma ku sha daga arziƙin Ubangijinku, kuma kada ku yi fasadi, a cikin ƙasa, kuna mãsu ɓarna."
Remember, when you said: "O Moses, we are tired of eating the same food (day after day), ask your Lord to give us fruits of the earth, herbs and cucumbers, grains and lentils and onions;" he said: "Would you rather exchange what is good with what is bad? Go then to the city, you shall have what you ask." So they were disgraced and became indigent, earning the anger of God, for they disbelieved the word of God, and slayed the prophets unjustly, for they transgressed and rebelled.
Kuma a lõkacin da kuka ce: "Yã Mũsã! Bã zã mu yi haƙuri ba a kan abinci guda. Sai ka rõƙa mana Ubangijinka Ya fitar mana daga abin da ƙasa take tsirarwa daga ganyenta, dumanta, da alkamarta da albasarta. Ya ce: "Kuna nẽman musanya abin da yake mafi ƙasƙanci da wanda yake mafi alhẽri? Ku sauka wani birni (daga cikin birane), lalle ne, kuna da abin da kuka rõƙa. "Kuma Muka dõka musu walãƙanci da talauci. Kuma suka kõma da wani fushi daga Allah. Wancan sabõda lalle su, sun kasance suna kãfirta da ãyõyin Allah, kuma suna kashe Aannabãwa, bãda hakki ba. Wancan, sabõda sãɓawarsu ne, kuma sun kasance suna ƙẽtarewar haddi.
Surely the believers and the Jews, Nazareans and the Sabians, whoever believes in God and the Last Day, and whosoever does right, shall have his reward with his Lord and will neither have fear nor regret.
Lalle ne waɗanda suka yi ĩmãni, da waɗanda suka tũba, da Nasãra da Makarkata, wana ya yi ĩmani da Allah da Yinin Lãhira, kuma ya aikata aikin ƙwarai, to, suna da ijãrarsu a wurin Ubangijinsu, kuma bãbu tsõro a kansu, kuma ba su zama suna yin baƙin ciki ba.
Remember the day We made the covenant with you and exalted you on the Mount and said: "Hold fast to what We have given you, and remember what is therein that you may take heed."
Kuma a lõkacin da Muka riƙi alƙawarinku, kuma Muka ɗaukaka dũtse a bisa gareku: "Ku kãma abin da Muka baku da ƙarfi. Kuma ku ambaci abin da yake a cikin sa, tsammãninku ku kãrekanku.
But you went back (on your word), and but for the mercy and grace of God you were lost.
Sa'an nan kuma kuka jũya daga bayan wancan, to, bã dõmin falalar Allah ba da rahamarSa a kanku, haƙĩƙa, dã kun kasance daga mãsu hasãra."
You know and have known already those among you who had broken the sanctity of the Sabbath, and to whom We had said: "Become (like) apes despised,"
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, kun san waɗanda suka ƙẽtare haddi daga gare ku a cikin Asabar, sai muka ce musu: "ku kasance birai ƙasƙantattu."
And whom We made an example for the people (of the day) and those after them, and warning for those who fear God.
Muka sanya ta (mas'alar) azãba, dõmin abin da yake gaba gareta, da yake a bãyanta, kuma wa'azi ga mãsu taƙawa.
Remember, when Moses said to his people: "God demands that you sacrifice a cow," they said: "Are you making fun of us?" And he said: "God forbid that I be of the ignorant."
Kuma a lõkacin da Musa yace ga mutanensa: "Lalle ne, Allah Yana umurtar ku da ku yanka wata sãniya." Suka ce: "Shin kana riƙon mu ne da izgili?" Ya ce: "Ina nẽman tsari daga Allah da in kasance daga jãhilai."
"Call on your Lord for us," they said, "that He might inform us what kind she should be." "Neither old nor young, says God, but of age in between," answered Moses. "So do as you are bid."
Suka ce: "Ka rõƙa mana Ubangijinka, Ya bayyana mana, mecẽ ce ita?" Ya ce: "Lalle ne, Shi, Yana cewa: "Lalle ne ita sãniya ce; bã tsõfuwa ba, bã kuma budurwa ba, tsakãtsaki ce a tsakãnin wancan,' sai ku aikata abin da ake umurninku."
"Call on your Lord," they said, "to tell us the colour of the cow." "God says," answered Moses, "a fawn coloured cow, rich yellow, well pleasing to the eye."
Suka ce: "Ka rõƙa mana Ubangijinka Ya bayyana mana abin da yake launinta." Ya ce: "Lalle ne, Shi Yana cewa: "Ita wata saniya ce fatsa-fatsa, mai tsan-tsan launi, tana faranta ran mausu kallonta."
"Call on your Lord," they said, "to name its variety, as cows be all alike to us. If God wills we shall be guided aright."
Suka ce: "Ka rõƙa mana Ubangijinka, Ya bayyana mana abin da yake ita, lalle ne shãnu suna yi mana kamã da jũna, kuma mu, idan Allah Yã so, haƙĩƙa, shiryuwa ne."
And Moses said: "He says it's a cow unyoked, nor worn out by ploughing or watering the fields, one in good shape with no mark or blemish." "Now have you brought us the truth," they said; and then, after wavering, they sacrificed the cow.
Ya ce: "Lalle ne Shi, Yana cẽwa: "Ita wata sãniya ce; ba horarra bã tana noman ƙasa, kuma ba ta shayar da shuka, lãfiyayya ce: bãbu wani sõfane a cikinta." Suka ce: "Yanzu kã zo da gaskiya. Sai suka yanka ta, kamar ba zã su aikata ba.
Remember when you killed a man and blamed each other for the deed, God brought to light what you concealed.
Kuma a lõkacin da kuka yi kisan kai, kuka dinga tunkuɗa wa jũna laifĩ a cikinsa, kuma Allah Mai fitar da abin da kuka kasance kuna ɓõyẽwa ne.
We had pronounced already: "Slay (the murderer) for (taking a life)." Thus God preserves life from death and shows you His signs that you may understand.
Sai Muka ce: "Ku dõke shi da wani sãshenta." Kamar wancan ne Allah Yake rãyar da matattu, kuma Ya nũna muku ayõyinSa, tsammãninku kuna hankalta.
Yet, in spite of this, your hearts only hardened like rocks or even harder, but among rocks are those from which rivers flow; and there are also those which split open and water gushes forth; as well as those that roll down for fear of God. And God is not negligent of all that you do.
San'nan kuma zukãtanku, suka ƙẽƙashe daga bãyan wancan. Sabõda haka suka zamanto kamar duwatsu. Ko mafi tsananin ƙeƙashewa. kuma lalle ne daga duwãtsu, haƙĩka, akwai abin da maremari suke ɓuɓɓuga daga gare shi, kuma lalle ne daga gare su, haƙĩƙa, akwai abin da yake tsatstsagewa har ruwa ya fita daga gare shi, kuma lalle ne, haƙĩƙa, daga gare su, haƙĩƙa, akwai da yake fãɗõwa dõmin tsõron Allah, kuma Allah bai zama gãfili ba daga barin abin da kuke aikatãwa.
How do you expect them to put their faith in you, when you know that some among them heard the word of God and, having understood, perverted it knowingly?
Shin fa kuna tsammãnin zã su yi imãni sabõda ku, alhãli kuwa, haƙĩƙa, wata ƙungiya daga gare su sun kasance suna jin maganar Allah, sa'an nan kuma su karkatar da ita daga bãyan sun gãne ta, alhãli sũ, suna sane?
For when they meet the faithful, they say: "We believe;" but when among themselves, they say: "Why do you tell them what the Lord has revealed to you? They will only dispute it in the presence of your Lord. Have you no sense indeed?"
Kuma idan sun haɗu da waɗanda suka yi ĩmãni sukan ce: "Mun yi ĩmãni," kuma idan sãshensu ya wõfinta zuwa ga sãshe, sukan ce: "Shin, kuna yi musu magana da abin da Allah Ya buɗa muku ne dõmin su yi muku hujja da shi a wurin Ubangijinku?" Shin fa, bã ku hankalta?
Do they not know that God is aware of what they hide and what they disclose?
Shin, kuma bã su sanin cẽwa lalle ne Allah Yana sanin abin da suke ɓõyẽwa da abin da suke bayyanãwa?
Among them are heathens who know nothing of the Book but only what they wish to believe, and are only lost in fantasies.
Kuma daga cikinsu akwai ummiyyai, bã su da sanin Littãfi, fãce tãtsuniyoyi, kuma sũ bã kõme suke yi ba fãce suna yin zato.
But woe to them who fake the Scriptures and say: "This is from God," so that they might earn some profit thereby; and woe to them for what they fake, and woe to them for what they earn from it!
To, bone ya tabbata ga waɗanda suke rubũta littãfi da hannuwansu sa'an nan kuma su ce wannan daga wurin Allah yake, dõmin su sayi kuɗi kaɗan da shi, san nan bone ya tabbata a gare su daga abin da hannayensu ke rubũtãwa, kuma bone ya tabbata a gare su daga abin da suke sanã'antãwa.
Yet they say: "The Fire will not touch us for more than a few days." Say.. "Have you so received a promise from God?" "Then surely God will not withdraw His pledge. Or do you impute things to God of which you have no knowledge at all?"
Kuma suka ce: "Wuta bã zã ta shãfe mu ba, fãce, 'yan kwãnuka ƙidãyayyu."Ka ce: "Ashe kun riƙi wani alkawari a wurin Allah, sa'an nan Allah ba zai sãɓa wa alkawarinSa ba ko kuwa kuna faɗin abin da ba ku sani ba bisa ga Allah?"
Why, they who have earned the wages of sin and are enclosed in error, are people of Hell, where they will abide for ever.
Na'am! Wanda ya yi tsiwur-wurin mũgun abu, kuma laifinsa ya kẽwaye shi, to, waɗannan su ne 'yan Wuta, sũ a cikinta madawwama ne.
But those who believe and do good deeds are people of Paradise, and shall live there forever.
Kuma waɗanda suka yi ĩmãni kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, waɗannan, 'yan Aljanna ne, sũ a cikinta madawwama ne.
Remember, when We made a covenant with the people of Israel and said: "Worship no one but God, and be good to your parents and your kin, and to orphans and the needy, and speak of goodness to men; observe your devotional obligations, and give zakat (the due share of your wealth for the welfare of others)," you went back (on your word), except only a few, and paid no heed.
Kuma a lõkacin da Muka karɓi alkawarin Bani-Isrã'ĩla: "Kada ku bauta wa kõwa fãce Allah, kuma ga mahaifa ku kyautata, da mai zumunta da marãyu da matalauta, kuma ku faɗi magana mai kyau zuwa ga mutãne, kuma ku tsayar da salla, kuma ku bãyar da zakka, sa'an nan kuka jũya bãya, fãce kaɗan daga gare ku, alhãli kuwa kuna mãsu bijirẽwa.
And remember, when We made a covenant with you whereby you agreed you will neither shed blood among you nor turn your people out of their homes, you promised, and are witness to it too.
Lõkacin da Muka riƙi alkawarinku; bã zã ku zubar da jininku ba, kuma bã zã ku fitar da kanku daga gidãjenku ba; sa'an nan kuka tabbatar alhãli kuwa kuna bãyar da shaida (a kanku).
But you still kill one another, and you turn a section of your people from their homes, assisting one another against them with guilt and oppression. Yet when they are brought to you as captives you ransom them, although forbidden it was to drive them away. Do you, then, believe a part of the Book and reject a part? There is no other award for them who so act but disgrace in the world, and on the Day of Judgement the severest of punishment; for God is not heedless of all that you do.
Sa'an nan kuma, gã ku, yã waɗannan! Kuna kashe kanku, kuma kuna fitar da wani ɓangare daga gare ku daga gidãjensu, kuna taimakon jũna a kansu da zunubi da zãlunci kuma idan kãmammu suka je muku kuna fansarsu alhãli kuwa shĩ fitar da su abin da aka haramta muku ne. Shin fa, kuna ĩmãni da sãshen Littãfin ne, kuma ku kãfirta da sãshe? To, mẽne ne sakamakon wanda ke aikata wancan daga gare ku fãce wulãkanci a cikin rãyuwar dũniya? Kuma a Rãnar ¡iyãma ana mayar da su zuwa ga mafi tsananin azãba. Kuma Allah bai zama Mai gafala ba daga barin abin da kuke aikatãwa.
They are those who bought the life of the world at the cost of the life to come; and neither will their torment decrease nor help reach them.
Waɗannan su ne waɗanda suka sayi rãyuwar dũniya da Lãhira, dõmin haka bã zã a sauƙaƙa azãba ba daga kansu, kuma sũ, bã ataimakonsu.
Remember We gave Moses the Book and sent after him many an apostle; and to Jesus, son of Mary, We gave clear evidence of the truth, reinforcing him with divine grace. Even so, when a messenger brought to you what did not suit your mood you turned haughty, and called some imposters and some others you slew.
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Munbai wa Mũsã Littãfi, kuma Mun biyar daga bãyansa da wasu Manzanni, kuma Muka bai wa Ĩsã ɗan Maryama hujjõji bayyanannu, kuma Muka ƙarfafa shi da Rũhi mai tsarki. Shinfa, kõ da yaushe wani manzo ya je muku tãre da abin da rãyukanku bã su so, sai ku kangara, wani ɓangare kun ƙaryata, kuma wani ɓangare kuna kashẽwa?
And they say: "Our hearts are enfolded in covers." In fact God has cursed them for their unbelief; and only a little do they believe.
Kuma suka ce: "Zukatanmu suna cikin rufi." A'a, Allah Yã la'ane su, dõmin kafircinsu kadan kwarai suke yin ĩmãni!
And when the Book was sent to them by God verifying what had been revealed to them already even though before it they used to pray for victory over the unbelievers and even though they recognised it when it came to them, they renounced it. The curse of God be on those who deny!
Kuma a lõkacin da wani Littãfi daga wurin Allah ya je musu, mai gaskatãwa ga abin da yake tãre da su, alhãli kuwa sun kasance daga gabãnin haka suna fãtar taimako da shi a kan waɗanda suka kãfirta. To, a lõkacin da abin da suka sani ya je musu, sai suka kãfirta da shi. Sabõda haka la'anar Allah ta tabbata a kan kãfirai.
They bartered their lives ill denying the revelation of God out of spite that God should bestow His grace among His votaries on whomsoever He will, and thus earned wrath upon wrath. The punishment for disbelievers is ignominious.
Tir, da abin da suka sayi rãyukansu da shi; watau su kãfirta da abin da Allah Ya saukar sabõda zãlunci; kada Allah Ya saukar da falalarsa a kan wanda Yake so daga bãyinsa. Sai suka kõmo da fushi game da wani fushi. Kuma ga kãfirai akwai azãba mai wulãƙantarwa.
And when it is said to them: "believe in what God has sent down," they say: "We believe what was sent to us, and do not believe what has come thereafter," although it affirms the truth they possess already. Say: "Why have you then been slaying God's apostles as of old, if you do believe?"
Kuma idan aka ce musu: "Ku yi ĩmãni da abin da Allah Ya saukar." Sai su ce: "Muna ĩmãni da abin da aka saukar a gare mu," kuma suna kãfircẽwa da abin da ke bãyansa, alhãli kuwa, shi ne gaskiyar (da suka sani) mai gaskatawa ga abin da yake tãre da su (na Attaura) Ka ce: "To, don me kuke kashe annabãwan Allah gabãnin wannan, idan kun kasance mãsu bãyar da gaskiya?"
Although Moses had come to you with evidence of the truth, you chose the calf in his absence, and you transgressed.
Kuma lalle ne haƙĩƙa Mũsã ya zo muku da hujjõji bayyanannu, sa'an nan kuka riƙi maraƙi (daga bãyansa, alhãli kuwa kuna mãsu zãlunci.
Remember when We took your pledge and exalted you on the Mount (saying:) "Hold fast to what We have given you, firmly, and pay heed," you said: "We have heard and will not obey." (The image of) the calf had sunk deep into their hearts on account of unbelief. Say: "Vile is your belief if you are believers indeed!"
Kuma a lõkacin da Muka riƙi alkawarinku kuma Muka ɗaukaka dutse a bisa gare ku, (Muka ce:) "Ku riƙi abin da Muka kãwo muku da ƙarfi kuma ku ji" Suka ce: "Mun ji kuma mun ƙi." Kuma aka zuba son maraƙin a cikin zukatansu sabõda kãfircinsu. Ka ce: "Tir da abin da ĩmãninku yake umurnin ku da shi, har idan kun kasance mãsu ĩmãni!"
README.md exists but content is empty. Use the Edit dataset card button to edit it.
Downloads last month
30
Edit dataset card